in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gobara ta lalata kayakin zabe yayin da ya rage kwanaki kalilan a gudanar da zaben shugaban kasa a Nijeriya
2019-02-13 10:53:37 cri
Yayin da ya rage kwanaki 4 gabanin zaben Shugaban kasa a Nijeriya, ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar INEC dake jihar Anambra, ya ce gobarar da ta tashi a ofishin ta lalata wasu daga cikin muhimman kayakin zabe.

Gobarar da ta tashi a babban ofishin INEC dake Akwa, babban birnin jihar, ta kama kwantainoni biyu dake dauke da na'urorin tantance masu kada kuri'a a zaben da za a yi ranar Asabar.

Kwamishinan INEC na jihar, Nwachukwu Orji da ya tabbatar da tashin gobarar, ya ce jami'an kwana-kwana da na tsaro ne suka yi nasarar kashe gobarar.

A cewar jaridar THISDAY ta kasar, gobarar ta tashi ne a daya daga cikin kwantainonin da ake amfani da su a matsayin ofishin wucin gadi a cikin hedkwatar hukumar dake jihar.

Sai dai jami'an tsaro sun hana 'yan jarida shiga harabar ofishin dan tantance irin asarar da gobarar ta haifar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China