in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Muhammadu Buhari: Matakan bunkasa tattalin arzikin Najeriya suna bada kyakkyawan sakamako
2019-02-10 16:34:17 cri
A jiya Asabar shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana a birnin Legas cibiyar kasuwancin kasar cewa, manufofin raya tattalin arziki da gwamnatinsa ta kaddamar suna samar da kyakkyawan sakamako, ya ce hakan ya bayyana a fili duba da yadda kasar ke samun bunkasuwar tattalin arziki sannu a hankali cikin shekaru ukun da suka gabata.

Shugaban na Najeriya ya bayyana hakan ne a lokacin wata ganawa da yayi da al'umma inda ya nanata alkawarin da ya dauka na cigaba da bunkasa tattalin arzikin kasar, ta hanyar toshe hanyoyin da kudaden gwamnatin kasar ke zurarewa, da kara samar da manyan ayyuka, kana da aiwatar da shirin farfado da tattalin arzikin kasar da na raya cigaban kasa.

Shugaba Buhari ya ce yayi amana cewa, zuba jari a fannin muhimman ayyukan more rayuwa zai kawowa kasar bunkasuwa.

Game da gina kyakkyawar makoma ga kasar kuwa, shugaba Buhari ya ce, gwamnatinsa za ta samar karin hanyoyin kudaden shiga domin bunkasa cigaban tattalin arzikin kasar da inganta tsarin aikin gwamnati ta hanyar tallafawa kamfanoni masu zaman kansu.

Shugaban na Najeriya ya fadawa kungiyar manyan 'yan kasuwa cewa, gwamnatinsa tana iyakar kokarinta wajen habaka tattalin arzikin kasar ta hanyar aiwatar da wasu sabbin shirye shirye da suka hada da shawo kan matsalolin tsaro da yaki da cin hanci da rashawa.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China