in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyyar adawa a Najeriya ta janye takara don marawa shugaban kasar baya don sake zabarsa a wa'adin mulki na biyu
2019-02-08 15:21:44 cri
Daya daga cikin jam'iyyun adawa a Najeriya ta sanar a jiya Alhamis cewa ta janye aniyar takararta a zaben shugaban kasar da za'a gudanar a ranar 16 da watan Fabrairu inda kuma ta mara baya ga shugaban kasar mai ci Muhammadu Buhari domin a sake zabarsa a wa'adin mulki karo na biyu.

Wannan ya biyo bayan matakin da kwamitin zartaswa na jam'iyyar (NEC) ta Social Democratic Party (SDP) ta yi ne a Abuja, babban birnin kasar.

A sanarwar da jam'iyyar ta fitar ta ce ta dauki matakin janyewa takarar ne sakamakon takaddama da doguwar shari'ar da ake fafatawa a tsakanin 'yan takarar jam'iyyar dake neman shugabancin kasar wato tsohon ministan yada labarai na Najeriyar Jerry Gana, da tsohon gwamnan jahar Cross River Donald Duke, wadanda suke son jam'iyyar ta SDP ta ba su takarar shugabancin Najeriya. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China