Dorcas Philemon, kakakin asibitin kwararru na jahar Taraba, ya tabbatar da mutuwar mutanen biyar ga manema labarai a Jalingo, babban birnin jahar.
Gidajen talabijin da shafukan sadarwa na zamani sun nuna dubban jama'a da suka yi dafifi a babban filin wasa dake Jalingo domin nuna goyon baya ga shugaba Buhari a lokacin da ya halarci jahar don kaddamar da gangamin yakin neman zabensa tare da wasu manyan jiga-jigan 'yan siyasa.
Sai dai shugaba Buhari, ya bayyana damuwa matuka sakamakon hasarar rayukan da aka samu a lokacin gangamin yakin neman zaben inji sanarwar da aka fitar. (Ahmad Fagam)