in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala taron AU da alkawarin yin aiki domin walwalar al'ummar Afrika
2019-02-12 11:48:13 cri

Shugaban Masar Abdel-Fattah al-Sisi, ya rufe taro na 32 na shugabannin kasashe da gwamnatoci mambobin Tarayyar Afrika AU, a hedkwatar kungiyar dake birnin Addis Ababa na Habasha, inda ya yi alkawarin yin aiki domin inganta walwalar al'ummar Afrika.

Abdel Fattah al-Sisi, wanda ya karbi shugabancin kungiyar na karba karba na tsawon shekara 1, daga shugaban Rwanda Paul Kagame, ya ce cikin shekara 1 mai zuwa, zai yi aiki tukuru wajen cimma muradun da AU ta fitar yayin taron, wadanda suka hada da fara aikin yankin ciniki cikin 'yanci na nahiyar da tsugunar da 'yan gudun hijira da kuma samar da aikin yi ga dimbin matasan nahiyar.

AU ta bayyana a ranar Juma'ar da ta gabata cewa, rikice-rikice daban daban a fadin nahiyar Afrika, sun raba mutane miliyan 20.8 da matsugunansu.

A cewar shugaba Al-Sisi, taron na AU karo na 32 mai take kan 'yan gudun hijira, ya bayyana yadda daidaitar jama'a ka iya haifar da kalubalen zamanta kewa da siyasa da tsaro da tattalin arziki a nahiyar, a don haka, zai mayar da hankali kan bangaren a cikin shekara 1 mai zuwa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China