in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron kolin AU ya tabo hanyoyin magance matsalar tsaro da tilastawa mutane ficewa daga muhallansu a Afrika
2019-02-11 11:31:32 cri

A yayin da aka bude taron kolin shugabannin kungiyar tarayyar Afrika AU karo na 32 a jiya Lahadi a Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha, muhimman batutuwan da suka kankane taron sun hada da matsalolin dake damun nahiyar kamar batun tilastawa mutane ficewa daga muhallansu da batun zaman lafiya da tsaro.

A jawabinsa na bude taron, shugaban kwamitin gudanarwar AU, Moussa Faki Mahamat, ya ce batun tilastawa jama'a kauracewa muhallansu na daya daga cikin abubuwan dake tayar da hankali a kasashen na Afrika.

"Abu mai muhimmanci shi ne a kara daukar matakai na shawo kan matsalar tun daga tushe, ta hanyar ayyukan hukumomin tallafawa rayuwar bil adama na Afrika," in ji Mahamat.

A lokacin bude taron, shugaban kasar Masar Abdel-Fattah al-Sisi ya karbi shugabancin taron kolin daga wajen Paul Kagame shugaban kasar Rwanda.

Da yake jawabi a lokacin taron, al-Sisi ya bukaci a kara kokari wajen bunkasa zaman lafiya da tsaro da tallafawa 'yan gudun hijira, bakin haure, da kuma mutanen dake rayuwar a sansanonin da aka kebewa mutanen da rikici ya tilastawa ficewa daga muhallansu.

Haka zalika ya jaddada bukatar a kara kaimi wajen yaki da ta'addanci da masu tsattsauran ra'ayin addini da kuma bunkasa muhimman kayayyakin more rayuwa da raya birane a nahiyar baki daya. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China