in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban jami'in AU ya yabawa dangantakar dake tsakanin Sin da Afrika a lokacin taron kolin AU
2019-02-11 10:07:58 cri
Moussa Faki Mahamat, shugaban gudanarwar kungiyar tarayyar Afrika (AU), ya nuna yabo game da hadin gwiwar dake tsakanin kungiyar tarayyar Afrika mai mambobi kasashen 55 da kasar Sin a fannoni daban daban.

Shugaban na AU ya bayyana hakan ne a lokacin bude taron kungiyar tarayyar Afirka karo na 32 a jiya Lahadi a Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha, wanda ya samu halartar shugabannin kasashen Afrika, da jami'an diflomasiyya, da sauran muhimman mutane.

Da yake jawabi game da dangantakar dake tsakanin AU da Sin, Mahamat ya ce, bangarorin biyu suna kara samun muhimman sauye sauye daga dukkan fannoni.

Nasarar da aka samu a taron dandalin hadin gwiwar Sin da Afrika (FOCAC) a Beijing a watan Satumbar 2018, ya kara bayyanawa a fili irin cigaban da ake samu game da batun dangantakar dake tsakanin bangarorin biyu.

A watan Satumbar 2018, AU ta kaddamar da ofishin wakilcinta a Beijing, inda ya bayyana cewa, matakin zai kara karfafa danganatakar dake tsakanin bangarorin biyu. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China