in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in AU ya yabawa kasar Sin bisa tallafawa bunkasuwar Afrika
2019-02-12 11:16:19 cri

Emmanuel Nnadozie, babban sakataren gidauniyar bunkasa cigaban Afrika (ACBF), a ranar Litinin ya yabawa irin tallafin da kasar Sin ke bayarwa wajen bunkasa cigaban nahiyar Afrika.

Nnadozie ya bayyana hakan ne ga kamfanin dillancin labarai na Xinhua, inda ya kara da cewa, "Mun jima muna sanya ido tare da nuna gamsuwa a fannonin daban daban na irin taimakon da gwamnatin kasar Sin ke bayarwa wajen bunaksa cigaban muhimman bangarorin da muke bukata,"

ACBF wata hukuma ce ta musamman mai fafutukar bunkasa cigaban kungiyar tarayyar Afrika AU.

Nnadozie ya kuma furta cewa, "Muna sane da irin dubban guraben karo ilmi da ake baiwa matasa 'yan kasashen Afrika domin yin karatu a kasar Sin kuma su koma gida Afrika bayan sun kammala domin taimakawa cigaban nahiyar."

Afrika ce babbar nahiyar da ta fi amfana daga tallafin raya cigaba na kasar Sin.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China