in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da a goyi bayan yaki da laifuffuka a kan teku
2019-02-06 15:17:14 cri
Wakilin dindindin na Sin a MDD Ma Zhaoxu, ya bukaci hadin kan dukkanin sassan masu ruwa da tsaki, wajen yaki da ayyukan bata-gari a sassan teku, yana mai cewa manyan laifuka da ake aikatawa a teku, na matukar barazana ga tattalin arziki a yankuna dake makwaftaka da gabobin tekun yammacin Afirka.

Ma Zhaoxu, ya yi wannan kira ne, yayin taron kwamitin tsaron MDD na jiya Talata, yana mai cewa Sin na iya kokarin ta, na taimakawa kasashen wannan yanki, wajen tsara manufofi, da hada sassan dabaru da ayyuka, domin karya lagon manyan laifuka da ake aikatawa a teku, matakin da zai kai ga samar da ci gaba, da wadata a kasashen shiyyar.

Kaza lika jami'in ya ce a shekarun baya bayan nan, duk da cewa an samu raguwar ayyukan 'yan fashin teku a zirin Aden, a hannu guda ana fuskantar matsalar tsaro a zirin Guinea dake yankin yammacin Afirka, wanda hakan ya yi matukar tasiri ga ci gaban tattalin arziki da zamantakewar kasashe masu makwaftaka da gabar tekun. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China