in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ba ta goyon bayan ayyukan sojojin haya a Afrika
2019-02-05 16:26:43 cri
Zaunanen wakilin kasar Sin a MDD Ma Zhaoxu, ya ce kasar Sin na adawa da ayyukan sojojin haya a Afrika, kuma za ta ci gaba da goyon bayan kokarin kasashen nahiyar na neman zaman lafiya da ci gaba.

Ma Zhaoxu wanda shi ne wakilin musammam na Shugaban kasar Sin Xi Jinping a wajen taron Kwamitin Sulhu na MDD kan ayyukan sojojin haya a Afrika, ya ce ayyukan sojojin haya na barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankalin kasashen Afrika, kuma kasar Sin na kira da kasashen duniya su kara kokarin magance matsalar.

Ya ce wadanan ayyukan na katsalandan ga harkokin cikin gidan kasashe masu tasowa da take cikakken iko da 'yancinsu, ya na mai cewa kasar Sin ba ta goyon bayan ayyukan ko kadan.

Wakilin na kasar Sin, ya kuma bukaci al'ummomin kasashen waje su taimakawa kasashen Afrika wajen gaggauta samun ci gaba da rage fatara da kawar da tushen matsalolin dake haifar da rikici da kuma inganta ci gaban tattalin arziki da zaman takewar kasashen nahiyar.

Ma Zhaoxu, ya kuma yi alkawarin Sin za ta ci gaba da marawa nahiyar Afrika baya, wajen samun zaman lafiya da kwanciyar hankali da ci gaba, inda ya bayyana fatan Sin da Afrika za su hada hannu wajen gina al'umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China