in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi kira da a kara yawan agajin ga 'yan gudun hijirar Nijeriya dake Kamaru
2019-02-05 16:23:23 cri
Kakakin MDD Stephanie Dujjaric, ya ce akwai bukatar hukumomin MDD da abokan huldarsu, su kara yawan agajin jin kai da suke kai wa 'yan Nijeriya dake gudun hijira a Kamaru.

Stephane Dujjaric ya ce ya kamata a kara agajin sosai ta yadda zai dace da mutane dake kara kwarara, inda wasu kuma suke kin komawa garin Rann ko sansaninsu dake Ngala, ba tare da samun tabbacin tsaro ba.

Yayin taron manema labarai da aka saba yi, Stephane Dujjaric ya shaidawa manema labarai cewa, ma'aikatan agaji na aiki tare da hukumomi, wajen kare hakkin 'yan gudun hijirar na samun mafaka tare da sauya musu matsuguni zuwa yankunan dake da tsaro, wadanda ke nesa da bakin iyakar kasar.

Kimanin 'yan gudun hijirar Nijeriya 35,000 ne suka tsere zuwa Kamaru. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China