in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi Allah wadai da katsalandan na kasashen waje a harkokcin cikin gidan Venezuela
2019-01-27 15:41:22 cri
Wakilin kasar Sin ya bayyana a jiya cewa gwamnatin Sin tana adawa da shisshigin da wasu kasashen duniya ke yi game da harkokin cikin gidan kasar Venezuela, a lokacin da wakilin na kasar Sin ke jawabi ga kwamitin tsaron sulhun MDD a wani taron gaggawa game da batun halin da ake ciki a kasar ta Venezuela.

"Kasar Sin a ko da yaushe tana adawa da yin katsalandan kan al'amurran da suka shafi cikin gidan wata kasa, kana tana Allah wadai da shisshigin da wasu kasahen duniya ke yi a harkokin cikin gidan kasar Venezuela," in ji Ma Zhaoxu, zaunannen wakilin kasar Sin a MDD.

Ba komai ba ne "halin da ake ciki a Venezuela ya shafi harkokin cikin gidanta ne," Ma ya ce, wannan batu "bai kasance barazana ga zaman lafiya da tsaron kasa da kasa ba, kuma ba wata ajanda ba ce da ta shafi kwamitin sulhun MDD."

"Kasar Sin tana adawa da sanya batun kasar Venezuela cikin ajandar kwamitin sulhun MDD," jakadan ya kara da cewa, harkokin kasar Venezuela al'ummar kasar ne kadai suke da ikon warware matsalarsu da kansu.

"Muna kira ga dukkan bangarorin da abin ya shafa da su mutunta zabin da al'ummar kasar Venezuelan suka yi wa kansu", in ji jakadan na kasar Sin. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China