in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in MDD ya bayyana damuwa game da hasarar da aka samu sanadiyyar ballewar dam a Brazil
2019-01-27 15:27:13 cri
Kakakin MDD ya bayyana a jiya Asabar cewa babban sakataren MDD Antonio Guterres, ya nuna damuwa dangane da hadarin ballewar dam a jihar Minas Gerais na kasar Brazil.

Babban jami'in MDD ya aike da sakon ta'aziyya ga iyalan wadanda hadarin ya rutsa da su, in ji Farhan Haq, mataimakin kakakin babban sakataren MDD.

"MDD a shirye take ta tallafawa hukumomin da abin ya shafa a kasar Brazil a kokarin da suke na aikin bada ceto da samar da kayan tallafi, in ji Haq.

A kalla mutane 34 ne aka bada rahoton mutuwarsu bayan madatsar ruwan mallakin kamfanin hakar ma'adanai Vale ya balle da yammacin ranar Juma'a a jahar Minas Gerais dake kudu maso gabashin kasar ta Brazil. Ballewar dam din ta haifar da gagarumar barna ga gidajen kwanan jama'a da yankin baki daya. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China