in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Sin ya yi kira da a kara azama wajen kyautata rayuwar al'umma
2019-02-03 16:13:05 cri
Firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya yi kira ga masu ruwa da tsaki da su kara azama, wajen aiwatar da manufofin gyare gyare a cikin gida da bude kofa ga kasashen waje, da bunkasa tsare tsaren tattalin arziki da na zamantakewa, ta yadda za a kai ga cimma nasarar kyautata rayuwar al'umma. Mr. Li Keqiang ya yi kiran ne, yayin da yake ziyara a yankin Mongolia ta gida dake arewacin kasar Sin tsakanin ranekun Juma'a da Asabar.

Firaministan na Sin, wanda kuma mamba ne a hukumar siyasa ta kwamitin kolin JKS, ya ziyarci gidajen mutane dake fama da talauci a garin Ulanqab.

Mr. Li ya bukaci sassa da batun ya shafa da su gudanar da bincike, su kuma zakulo hanyoyin bunkasa noman dankali a yankin, a wani mataki na yaki da fatara ta hanyar inganta aikin noma.

Yayin ziyararsa wata kasuwa ta manoma, Li ya ganewa idanunsa yanayin ciniki, da farashin naman shanu da na awaki. Ya ce ya zama wajibi a dauki matakan yawaita kudaden shigar al'umma, ta yadda za su samu damar kashe karin kudade. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China