in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta daidaita bunkasuwar tattalin arzikinta bisa matsakaicin matsayi
2019-01-16 20:33:46 cri
Firaministan kasar Sin Li Keqiang ya bayyana cewa, kasarsa za ta ci gaba da kirkiro tare da inganta manufofinta na sanya ido don magance matsalolin da ka iya kunno kai, za kuma a ci gaba da daidaita ci gaban tattalin arzikin kasar bisa matsakaicin matsayi.

Li ya bayyana hakan ne yayin da yake jagorantar taron karawa juna sani, inda ya saurari ra'ayoyi da shawarwari da masana da masu masana'antu suka gabatar game da daftarin rahoton aikin gwamnati.

Li, kana mamban zaunannen kwamitin hukumar siyasa na kwamitin kolin JKS, ya bayyana cewa, kasar Sin za ta hanzarta farfado da shirinta na raya kasa da zurfafa yin gyare-gyare da bude kofa ga kasashen waje da zurfafa samun ci gaba mai inganci.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China