Wata sanarwa da IOM ta fitar, ta ce ya zuwa ranar Laraba, tawagar masu aikin ceton bakin hauren, ta gano 52 daga wadanda hadarin ya rutsa da su. A ranar Talata an gano wasu maza uku da mata biyu, kana a Laraba aka gano gawawwakin mutane 47.
Sanarwar ta ce akwai kuma mutane 16, da suka tsallake rijiya da baya a Obock, dake bakin tekun na Djibouti. (Saminu Hassan)