in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bude sansanin sojojin na farko a kasashen waje
2017-08-02 09:17:34 cri
A jiya ne aka yi bikin bude sansanin sojojin 'yantar da jama'a na kasar Sin (PLA) a kasar Djibouti, wanda shi ne sansanin soja na farko da kasar Sin ta bude a ketare.

Manufar bude wannan sansanin dai, ita ce baiwa kasar Sin damar sauke nauyin dake kanta a harkokin kasa da kasa, musamman ba da agajin jin kai da kuma yiwa jiragen ruwa dake zirga-zirga a yankin ruwayen Somaliya da tekun Aden rakiya.

A ranar 11 ga watan Yulin wannan shekara ce aka kafa sansanin sojojin PLA a kasar Djibouti, bisa shawarar kasashen Sin da Djibouti, zai kuma taimakawa kasar Sin cika alkawuranta kan harkokin kasa da kasa.

An gudanar da fareti tare da kafa tutar kasar Sin yayin wannan biki da ya gudana a barikokin sansanin sojojin na PLA. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China