Kwamandan hukumar 'yan sandan birnin Nairobi, Philip Ndolo ya ce, wani keke tura kaya da wani mutum da ba'a san kowane ne ba ya karbi hayarsa domin dibar jakankunansa a tsakiyar birnin yana dauke da abubuwan fashewa a cikinsa, ya yi matukar jikkata mutumin dake tura kayan. Da kuma wani mutumin dake wucewa ta kusa da inda lamarin ya auku shi ma ya samu kananan raunuka.
'Yan sanda sun garzaya da wadanda suka jikkatan zuwa asibiti. "Akwai kuma masana kan boma bomai a wajen," in ji Ndolo.
Mai tura keken daukar kayan ya ce, kayan sun fashe ne mintoci 10 bayan da mutumin da ya dauki hayar tasa ya tafi wani waje da nufin dauko katinsa na shaida wanda ya yi ikirarin cewa ya manta da katin nasa. Ya bayyana hakan ne ga 'yan jaridu bayan an garzaya da shi asibitin. (Ahmad Fagam)