in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Kenya: Mutane 14 ne suka mutu a harin da aka kai kan wani Otel a Nairobi
2019-01-16 19:57:29 cri
Shugaba Uhuru Kenyatta na kasar Kenya ya tabbatar a yau Laraba cewa, mutane 14 ne aka kashe wasu da dama kuma suka jikkata, bayan wani mummunan hari da aka kai kan wani otel da rukunin kasuwanci da baki 'yan kasashen waje ke yawan zuwa a Nairobi,babban birnin kasar.

Kenyatta ya bayyana ta kafar talabijin cewa, an kawo karshen matakan tsaron da aka kaddamar kana an kashe dukkan 'yan ta'addan da suka kai hari a harabar otel din DusitD2, lamarin da ya kawo karshen sa'o'i 18 na harin ta'addancin da aka kai a babban birnin kasar.

Shugaban ya kuma lashi takobin karfafa matakan yaki da ayyukan ta'addanci a duniya, yana mai cewa, 'yan ta'adda ba za su taba samun galaba a kan mu ba.

Rundunar 'yan sandan kasar Kenya ta bayyana cewa, 'yan ta'adda shida ne suka kaddamar da harin. Kungiyar 'yan ta'adda ta al-Shabaab dake Somaliya ta dauki alhakin kaddamar da harin.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China