in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Kenya ta lashi takwabi karfafa matakan yaki da ayyukan ta'addanci
2019-01-18 20:25:32 cri
Sakatariyar a ma'aikatar harkokin wajen kasar Kenya Monica Juma ta bayyana kudurin kasarta na karfafa matakan yaki da ayyukan ta'addanci da kara hada kai da kasashen duniya don murkushe tsattsauran ra'ayi.

Kalaman jami'ar kasar ta Kenya na zuwa ne kwanaki uku bayan harin da a kai kan wani otel dake da rukunin shaguna a Nairobin kasar Kenya.

Monica Juma ta kuma bayyana kudurin kasar ta Kenya na yaki da duk wani nau'i na ta'addanci, tana mai cewa, jami'an tsaro za su bankado tare da hukunta duk wadanda ke da hannu cikin harin na Nairobi da ya yi sanadiyar rayukan mutane 21 kana wasu da dama kuma suka jikkata.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China