in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Najeriya ta yi zargin barazanar tsaro a babban zaben kasar dake tafe
2019-01-22 10:20:41 cri
A jiya Litinin gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa tana zargin akwai barazanar tsaro a babban zaben kasar dake tafe, inda ta yiwa al'ummar kasar ta yammacin Afrika gargadi da su yi taka tsantsan game da fargabar da ake da shi na yiwuwar kai hare hare kafin zaben, lokacin zaben da kuma bayan zaben.

Gwamnatin ta ce, ta samu wasu sahihan bayanai dake tabbatar da cewa wasu daga cikin 'yan adawar siyasa suna ta yunkurin haddasa tashe-tashen hankula a duk fadin kasar domin kawo cikas ga zaben kasar wanda za'a fara a watan gobe.

Da yake jawabi ga 'yan jaridu, ministan yada labaran Najeriyar Lai Mohammed ya ce, gwamnati ta samu wasu sahihan bayanai dake cewa mayakan 'yan tada kayar baya da na Boko Haram suna shirye-shiryen kaddamar da munanan hare-hare da ta da hargitsi a wasu jahohin kasar.

Kakakin gwamnatin Najeriyar ya ce, akwai wasu jahohin arewaci da tsakiyar Najeriyar da ake son kaddamar da hare-haren

Babbar jam'iyyar adawar kasar (PDP), tun a ranar Lahadin da ta gabata ta yi gargadi cewa akwai tashe-tashen hankula a wasu daga cikin jihohin Najeriyar, gabanin gudanar da zabukan kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China