in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya ya yi Allah wadai da harin ta'addanci a kasar Kenya
2019-01-18 09:25:21 cri
Shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari ya yi Allah wadai da mummunan harin ta'addanci wanda aka kaddamar kan wani otel da rukunun shaguna a Nairobi.

A sakon ta'aziyyar da ya aiki a Abuja, babban birnin Najeriya a ranar Laraba, shugaban Najeriya ya jajantawa gwamnati da al'ummar kasar Kenya, inda ya bayyana harin da cewa mummunan laifi ne, wanda wasu mutane bata gari suka aikata.

Buhari ya bukaci al'ummar kasashen duniya da su tallafawa kasar ta Kenya domin kawo karshen karuwar ayyukan ta'addanci a kasar, a cewar shugaban " duk wani harin ta'addanci da aka kaddamar kan wata kasa guda daya tamkar hari ne kan dukkan kasashen duniya."

Adadin mutanen da suka mutu a sanadiyyar harin ta'addancin da aka kaddamar kan otel da manyan shagunan a Nairobi ranar Talata ya kai mutuna 21, hukumar 'yan sanda kasar ne ta sanar a daren ranar Laraba.

Kungiyar mayakan 'yan ta'adda ta al-Shabab dake da sansaninta a kasar Somalia ta dauki alhakin kai harin. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China