in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bangarorin da ba sa ga maciji da juna a Tripoli sun sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya
2019-01-22 09:33:52 cri
A jiya Litinin bangarorin da ba sa ga maciji da juna a Tripoli na kasar Libya sun amince da sanya hannu kan yarjejeniyar tsakaita bude wuta bayan wata tattaunawar shiga tsakani, gidan talabijin na kasar ne ya sanar da hakan.

Mohamed al-Barghuthi, shugaban tawagar wakilai masu shiga tsakani, shi ne ya bayyana hakan ga manema labarai bayan sanya hannu kan yarjejeniyar tsakaita bude wutar, "an kuma amince da bude wasu hanyoyi da aka riga aka rufe kuma an bude shingen dake hana al'umma sukuni, da musayar fursunoni da wadanda ake tsare da su, don tabbatar da aiwatar da yarjejeniyar, da kawo karshen kariyar da al'umma da sojoji ke baiwa bata gari."

Wakilin musamman na MDD a Libya Ghassan Salame, ya yabawa yunkurin da masu shiga tsakanin suka yi, inda ya yi fatan samun cikakkiyar aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma matsaya kanta," ofishin wanzar da zaman lafiya na MDD a Libya shi ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa.

Kudancin Tripoli ya jima yana fuskantar tashe-tashen hankula musamman a cikin 'yan kwanakin da suka gabata tsakanin dakarun dake biyayya ga gwamnati da kungiyoyin masu dauke da makamai da ake kira da suna Seventh Brigade. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China