"Jirgin ruwan mai suna Atlantis, yana dauke da tutar kasar Liberia yana tangal-tangal sakamakon matsalar da yake fuskanta a tekun saboda tsananin kadawar igiyar ruwa a lokacin da jirgin ruwan ke kokarin shiga tashar ruwan Tripoli," ofishin tattara bayanai na sojojin ruwan kasar Libyan ne ya sanar da hakan.
Jirgin ruwan ya bugi wani dutse inda ruwa ya taba injinsa, a cewar sanarwar.
Dukkan matuka jirgin su 14 a ceto su, wadanda dukkansu Indiyawa ne. (Ahmad Fagam)