in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Libya: MDD ta yaba da sakin mutane da dama wadanda IS ta yi garkuwa da su
2019-01-02 09:48:42 cri
Tawagar MDD mai aikin wanzar da zaman lafiya a kasar Libya ko UNSMIL a takaice, ta yaba da sakin mutane 20 da kungiyar IS ta yi garkuwa da su a Fug'ha da Tazirbu dake kudancin kasar.

Wata sanarwa da UNSMIL din ta fitar, ta ce hakan wata kakkarfar alama ce da ke nuna cewa, muddin al'ummar Libya suka hada karfi da karfe, suna iya murkushe kungiyar IS, tare da shawo kan tarin kalubale dake addabar kasar.

Kakakin rundunar sojojin kasar mai helkwata a gabashi Ahmad al-Mesmari ya tabbatar da cewa, sojoji sun kaddamar da hare-hare kan mayakan IS dake yankunan kudancin kasar, inda suka kubutar da mutane da dama da kungiyar ke tsare da su.

A watan Nuwambar shekarar da ta shude ne dai dakarun kungiyar IS suka kaddamar da samame a wasu ofisoshin 'yan sanda, da gine-ginen gwamnati dake Tazirbu, inda suka hallaka mutane takwas, suka raunata wasu 15, kana suka yi awon gaba da wasu da dama.

A watan Oktoba kuma mayakan suka farwa garin Fug'ha dake gundumar Jufra, mai nisan kilomita 650 kudu maso gabashin birnin Tripoli, inda suka hallaka mutane biyar, kana suka sace wasu mutanen da dama. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China