in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan majalissar Birtaniya sun yi watsi da sharuddan ficewar kasar daga tarayyar Turai
2019-01-16 10:24:00 cri
'Yan majalissar dokokin Birtaniya, sun yi watsi da sharuddan ficewar kasar daga tarayyar Turai ta EU da firaministan kasar Theresa May ta gabatar musu, matakin da ya kara dagula matakan kasar na ficewa daga EUn.

A jiya Talata ne mambobin majalissar sun jefa kuri'un amincewa da sharuddan 202, da kuma na kin amincewa da su 432, bayan kwashe kwanaki biyar ana tafka muhawara. Manazarta dai na cewa wannan ne karon farko da gwamnatin kasar ta fuskanci rashin nasara mafi tsanani tun bayan shekarun 1920.

Firaministar Birtaniya Theresa May na da kwanaki uku, kafin komawa majalissar da wani tsarin na daban, domin neman amincewarsu. Bisa tsarin da ake da shi a kasa, Birtaniya za ta kammala ficewa daga tarayyar Turai ne a ranar 29 ga watan Maris mai zuwa.

Da take tsokaci game da halin da ake ciki, uwargida May, ta ce duk kwanan duniya kasar tana kara shiga rudani, muddin ba a kai ga warware matsalar da ake ciki ba.

Shi kuwa wani masani game da siyasar kasar Dr. Alan Wager, cewa ya yi sakamakon da ya tabbatarwa gwamnatin kasar rashin nasara, ya wuce wanda aka yi tsammani, kana hakan ya jefa kasar cikin wani yanayi na babban rashin tabbas. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China