in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha ba za ta lamunci matsin lamba daga Birtaniya game da hari kan 'dan leken asiri ba
2018-03-15 10:59:38 cri
Ma'aikatar harkokin wajen kasar Rasha, ta ce ko kadan kasar ba za ta lamunci duk wani mataki na horo da Birtaniya za ta dauka kan ta ba, bisa zargi cewa wai Rashan ce ta sanyawa wani 'dan leken asirin kasar mai cin tudu biyu guba.

Wata sanarwa da ma'aikatar ta dora kan shafin ta na yanar gizo, ta yi kakkausan suka game da furucin firaministar Birtaniya Theresa May, na zargin Rasha da sanyawa 'dan leken asiri Sergei Skripal da 'yar sa guba. Rasha ta kuma alkawarta daukar matakin gaggawa na hukunci kan hakan.

Sanarwar ta ce kalaman firaminista Theresa May na ranar 14 ga wata sun sabawa ka'idar zaman jituwa dake wanzuwa tsakanin kasashen biyu.

Sanarwar ta kara da cewa, sakamakon amfani da hanyar bincike maras tsari, Birtaniya ta sake daukar mataki na nuna kin jinni ga Rasha. Har wa yau Rasha ta ce ba za ta lamunci matakan da Birtaniya ta fara dauka a kan ta ba, wadanda ke da nasaba da cimma muradun siyasa masu kunshe da nuna tsana da muzugunawa, ciki hadda matakin korar jami'an diflomasiyyar Rasha su 23 daga Birtaniya.

Daga karshe sanarwar ta tabbatar da cewa, Rasha za ta gaggauta daukar matakan ramuwar gayya ba tare da wani jinkiri ba. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China