Direban babbar motar, wanda ya dauko buhunan shinkafa, ya gaza sarrafa motar ne inda kuma motar ta kwace zuwa cikin wata babbar kasuwa ta Iworoko, kamar yadda Caleb Ikechukwu, kakakin hukumar 'yan sandan jihar Ekiti ya tabbatar da hakan.
Shaidun gani da ido sun fadawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, sun ga gawarwakin mutane a kalla 20 bayan da jami'an aikin ceto suka tattaro su.
Wani da ya ganewa idonsa faruwa lamarin mai suna Bisi Ayedun, ya ce yawancin wadanda hadarin ya rutsa da su 'yan kasuwa ne dake saye da sayarwa a wajen kasuwar. (Ahmad Fagam)