Mai magana da yawun sojojin saman kasar Ibikunle Daramola wanda ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa, ya ce, an kai samamen na ranar Jumma'a da jijjifi ne, sakamakon wasu rahotannin sirri da ke nuna cewa, mayakan na amfani da wuraren wajen kaddamar da hare-hare.
Sanarwar ta kara da cewa, daga bisani sojojin kasa sun mamaye maboyar mayakan inda suka yi nasarar gano Babura da 'yan ta'addan suka bari.
Daruruwan mutane ne dai suka rasa rayukansu a hare-haren dake da nasaba da gungun 'yan ta'addan cikin wannan shekarar kadai a jihar ta Zamfara dake yankin arewa maso yammacin kasar. (Ibrahim Yaya)