in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tanzania ta alkawarta bunkasa hadin gwiwa da hukumar UNHCR
2019-01-14 09:37:14 cri
Gwamnatin kasar Tanzania ta sha alwashin bunkasa hadin gwiwa da hukumar MDD mai lura da 'yan gudun hijira ko UNHCR, wajen samar da matsuguni ga masu neman mafaka, da 'yan gudun hijira na al'ummu makwaftan kasar.

Ministan cikin gidan kasar Kangi Lugola, shi ne ya bayyana hakan a jiya Lahadi, yayin ganawa da wakilin UNHCR na Tanzania Chansa Kapaya. Jami'an biyu sun tattauna game da batutuwan da suka shafi 'yan gudun hijira, da yadda Tanzania za ta ci gaba da hadin gwiwa da hukumar ta MDD, karkashin tanajin dokoki da ka'idojin kasa da kasa.

Mr. Lugola ya ce mawuyaci ne Tanzania ta cimma nasara a fannin tallafawa, da tsugunar da 'yan gudun hijira, ba tare da hadin gwiwar UNHCR ba. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China