in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tanzania ta bukaci mambobin AU da su gabatar da tallafin su a kan lokaci
2018-08-28 10:38:29 cri
Mataimakiyar shugaban kasar Tanzania Samia Suluhu Hassan, ta yi kira ga kasashe mambobin kungiyar hadin kan Afirka ta AU, da su gabatar da tallafin da suka alkawarta a kan lokaci, domin baiwa kungiyar damar gudanar da ayyukan ta yadda ya kamata.

Samia wadda ta yi wannan kira, jim kadan da rantsar da sabbin masu shari'a 3 a birnin Arusha, ta ce wasu hukumomin kungiyar ta AU, kamar kotun lura da hakkokin bil Adama ta AFCHR, sun shiga wani yanayi sakamakon karancin kudaden gudanarwa.

Jami'ar ta kara da cewa, ya dace ko wace kasa ta gabatar da tallafin ta a kan lokaci, ganin cewa kasashe da dama sun sanya hannu kan yarjejeniyar samar da tallafin kudade, wadanda za su ba da damar ci gaba da ayyuka, maimakon dogaro da hukumomin wajen nahiyar dake samar da taimako.

Uwargida Samia ta ce gwamnatin Tanzania, wadda daya ce cikin sassa da suka sanya hannu kan yarjejeniyar kafa kotun, ta alkawarta ci gaba da hadin gwiwa domin cimma nasarar ayyukan ta. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China