in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tanzania ta jinjinawa Sin bisa gudummawar guraben karatu
2018-08-13 09:41:34 cri
Ministan ma'aikatar ilimi kimiyya da fasaha na kasar Tanzania Joyce Ndalichako, ya yabawa kasar Sin, bisa tallafin da take baiwa kasar sa a fannin samar da guraben karo ilimi ga dalibai, da horon sanin makamar aiki ga jami'an lafiya.

Joyce Ndalichako ya bayyana hakan ne a jiya Lahadi, yayin bikin ban kwana da daliban da suka samu irin wannan dama, wanda ya gudana a birnin Dar es Salaam.

Ministan ya ce Sin ta nunawa duniya matsayinta na kasancewa abokiya ta gari, ta hanyar tallafawa Tanzania a fannoni da dama, ciki hadda hanyar bunkasa ilimi da horas da jami'an kasar. Ya ce yana farin cikin ganin kasarsa ta samu wannan dama, duba da cewa jami'an da za su samu horo a kasar Sin sun fito ne daga sassan da ake matukar bukatar hidimar su.

Jami'an lafiya da za su samu horo karkashin wannan dama da Sin ta tanadarwa Tanzania a wannan karo, sun hada da ma'aikatan lafiya masu aikin dashen bargo, da masu dashen koda, da kwararru a fannin kula da lafiyar jini, da masana fannin likitancin magunguna. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China