in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Masar ya ce akwai bukatar kara hada gwiwar kasashen Afirka don neman samun bunkasuwa
2018-12-10 10:56:20 cri
Shugaban kasar Masar Abdel Fattah al-Sisi ya ce a halin yanzu akwai matukar bukatar kasashen Afirka su rubanya kokarin yin hadin-gwiwa da dunkule tattalin arzikinsu daga matakai daban-daban.

Tuni a ranar Asabar, aka bude taron dandalin tattaunawa tsakanin kasashen Afirka na shekara ta 2018 a birnin Sham el-Sheikh dake bakin tekun Bahar Maliya wato Red Sea na Masar, wanda ya samu halartar shugabannin kasashe membobin kungiyar kawancen kasashen gabashi da kudancin Afirka ta samar da yankin ciniki cikin 'yanci ko kuma COMESA a takaice, inda shugaba Sisi ya ce kasashen duniya na ganin Afirka a matsayin nahiya mai cike da kyawawan damammaki, wadda ta cancanci cimma burin neman ci gaban tattalin arziki mai dorewa.

Sisi ya kuma kara da cewa, Afirka na da albarkar yawan jama'a da arziki, wanda kuma kalubale ne na samun zaman rayuwa mai kyau ga dukkanin jama'ar nahiyar.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China