in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masar ta samu iznin daukar bakuncin shirya gasar cin kofin Afirka ta shekarar 2019
2019-01-09 10:59:51 cri
Rahotanni daga gidan telebijin na kasar Masar na cewa, hukumar kwallon kafa ta nahiyar Afirka ta sanar a jiya cewa, kasar Masar ce za ta karbi bakuncin shirya gasar cin kofin kwallon kafan Afirka ta shekarar 2019.

A watan Yunin shekarar 2019 ne, za a gudanar da gasar cin kofin kwallon kafan Afirka, gasar da ake sa ran kasashe 24 na nahiyar za su halarta a wannan karo.

Kafin hakan, an soke iznin daukar bakuncin shirya gasar da a baya aka baiwa kasar Kamaru, saboda hukumar kwallon kafa ta nahiyar Afirka tana ganin cewa, kasar Kamaru ba za ta iya shirya gasar kamar yadda ake bukata ba, daga baya ne kasashen Masar da Afirka ta Kudu suka nuna aniyarsu ta karbar bakuncin gasar.

Kasar Masar ta taba zaman zakara sau 7 a tarihi a gasar cin kofin kwallon kafan Afirka. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China