in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kotun kolin Madagascar ta amince da sakamakon zaben shugaban kasar
2019-01-09 13:55:22 cri
Kotun kolin tsarin mulkin kasar Madagascar ta amince da sakamakon zaben shugaban kasar zagaye na biyu, wanda Andry Rajoelina ya lashe a wannan karo.

A ranar 27 ga watan Disamban bara ne, hukumar zaben kasar Madagascar ta sanar da sakamakon kuri'un zaben shugaban kasar zagaye na biyu, inda Andry Rajoelina ya samu kashi 55.66 cikin dari, ya doke Marc Ravalomanana, abin da ya ba shi damar lashe zaben.

Bayan da hukumar zaben kasar Madagascar ta sanar da sakamakon zaben ne, magoya bayan Ravalomanana suka yi zanga-zanga cewa, an tabka magudi yayin da jefawa da ma kidaya kuri'un a zagaye na biyu, tare da kin amincewa da sakamakon zaben. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China