in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabanni a Madagascar sun yi kira da a hadda hannu wajen dakatar da rikicin siyasa
2018-03-30 13:34:37 cri
Shugbanni a Madagascar sun yi kira da a hada hannu wajen dakatar da rikicin siyasa da yaki ci yaki cinyewa a kasar.

Shugabannin sun yi kiran ne yayin bikin cika shekaru 71 na barkewar rikicin nuna adawa da mamayar Faransa a kasar.

An gudanar da bukukuwa da dama a fadin kasar don tunawa da dubban mutanen da yakin ya rutsa da su.

A birnin Moramanga dake da nisan kilomita 110 daga babban birnin kasar Antananarivo, shugaban kasar Hery Rajaonarimampianina ya gudanar da bikin ajiye furanni a inda aka binne daruruwan 'yan kasar a makabartar wadanda suka sadaukar da kansu.

A cewar Shugaban, fadan da mazan jiyan suka yi ya nuna cewa hadin kai na da muhimmanci wajen ceton kasar.

A ranar 29 ga watan Maris din 1947 ne fadan nuna kin jinin Faransa ta barke a fadin Madagascar, inda rikicin ya fi kamari a birnin Moramanga. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China