Hukumar ta bayyana cikin wata sanarwa cewa, yanzu haka ana tattaunawa a kan daftarin kundin tsarin mulkin kasar. Sanarwar hukumar dai na zuwa ne bayan da shugaban hukumar zaben kasar Imad Al-Sayah ya sanar da cewa, za a shirya kuri'ar raba gardama game da kundin tsarin mulkin kasar na din-din-din kafin karshen watan Fabrairun shekarar 2019 dake tafe. (Ibrahim)