Rahotanni sun ce masu zanga zangar sun kunshi abokai ko 'yan uwan wadanda suka jikkata, da ma wadanda suka rasa rayukansu, yayin juyin juya halin kasar, inda suka rika bayyana bukatunsu na biyan albashi, da kudaden magani ga wadanda lamarin ya shafa.
An ce wani sashe na dandazon masu zanga zangar sun karya kofar helkwatar suka kuma shiga cikin ta. Daga bisani mataimakin firaministan kasar Ahmad M'etig, ya zanta da su, tare da sauraron bukatunsu.
Wata kafar watsa labarai dake birnin ta wallafa hotunan masu zanga zangar dauke da alluna masu kunshe da bukatun su, wasun su a cikin helkwatar gwamnatin, wasu kuma a farfajiyarta. (Saminu Hassan)