in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan bindiga sun kashe mutane 17 a arewacin Najeriya
2018-12-24 09:13:07 cri
Hukumar 'yan sanda a Najeriya ta ce kimanin mutane 17 ne aka tabbatar da mutuwarsu bayan wani hari da 'yan bindiga da ba'a gano ko su wanene ba suka kaddamar a jahar Zamfara dake shiyyar arewa maso yammacin kasar.

Harin wanda aka kai da yammacin ranar Asabar a kauyen Magami dake gundumar Faru a karamar hukumar Maradun na jahar Zamfara, harin ya zo ne kasa da mako guda bayan wani harin da aka kai wani yanki dake jahar wanda ya yi sanadiyyar rayukan mutane 25.

Kakakin hukumar 'yan sandan jahar Zamfara Muhammed Shehu, ya ce an tura karin jami'an 'yan sanda zuwa yankin domin hana sake kaddamar da wani harin a yankin.

Jami'an gwamnati da dama, har da mukaddashin gwamnan jahar Zamfara, Sanusi Rikiji, sun halarci jana'izar wadanda harin ya rutsa da su a jiya Lahadi. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China