in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masu sa ido a yarjejeniyar zaman lafiyar Sudan ta kudu sun yi tir da hari kan tawagar zaman lafiya
2018-12-24 09:54:04 cri
Masu sa ido kan shirin zaman lafiyar Sudan ta kudu sun yi Allah wadai da harin da aka kaddamar kan ma'aikatan dake kula da shirin yarjejeniyar tsakaita bude wuta da masu aikin tantancewa a yankin Luri, dake yammacin Juba, babban birnin kasar, a ranar 18 ga watan Disamba wanda dakarun tsaron gwamnati suka kaddamar.

Hukumar hadin gwiwa mai sanya ido da bin diddigi (RJMEC) ta bukaci a gudanar da cikakken bincike game da harin da aka kaddamar kan tawagar jami'an dake sanya ido kan yarjejeniyar tsagaita bude wuta dake kasar (CTSAMVM).

"Muna sa ran gwamnati za ta gudanar da cikakken bincike na adalci ba tare da bata lokaci ba, kuma wadanda aka samu da hannu a gurfanar da su gaban shari'a," masu sanya idon ne suka bayyana cikin wata sanarwar da aka fitar a Juba.

Masu sanya idon sun bukaci gwamnati da ta dauki matakan da suka dace wajen hana sake afkuwar hakan a nan gaba, a yayin da shirin wanzar da zaman lafiyar kasar Sudan ta kudu ke ci gaba da gudana. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China