Harin na ranar Laraba da maharan suka kai a yankin, shi ne na baya-bayan a jerin hare-haren da 'yan bindiga ke kaiwa yankin arewa maso yammacin kasar cikin watanni 6 da suka gabata.
Mazauna yankin sun bayyana cewa, galibin wadanda harin ya rutsa da su, suna aikin tsintar tunatur ne a gonakansu, lokacin da 'yan bindigar suka farma musu, suna harbin kan mai uwa da wabi. (Ibrahim)