Rahotanni sun ce 'yan bindigar sun hallaka Mr. Badeh ne da daren ranar Talata, bayan da suka tare motar da yake ciki suka kuma bude masa wuta.
Badeh, ya taba rike mukamin babban hafsan hafsoshin Najeriya, da mukamin babban hafsan rundunar sojojin saman kasar.
Cikin wasu sakwanni da kakakin rundunar sojojin saman Najeriya Ibikunle Daramola ya wallafa a shafin sa na tweeter, ya ce marigayin na dawowa daga gonar sa ne, lokacin da maharan suka tare shi a hanyar Keffi zuwa Abuja inda kuma suka harbe shi da bindiga.
Wata majiya ta ce maharan sun kuma hallaka wasu mutanen biyu baya ga Mr. Badeh. (Saminu)