in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojin Najeriya ta dage takunkumin haramtawa UNICEF aiki a arewa maso gabashin kasar
2018-12-16 16:26:37 cri
Rundunar sojojin Najeriya ta sauya matsayinta game da haramtawa asusun tallafawa ilmin kananan yara na MDD wato (UNICEF) gudanar da ayyukanta a shiyyar arewa maso gabashin kasar.

Hukumar sojin ta sauya tunaninta ne bayan wani taron ganawa da ta gudanar da masu ruwa da tsaki da kuma wasu muhimman mutane a Najeriyar, Onyema Nwachukwu, shi ne kakakin rundunar sojojin kasar ya bayyana hakan cikin wata sanarwar da aka baiwa kofenta ga kamfanin dillancin labarai na Xinhua a jiya Asabar.

Rundunar sojojin ta zargi hukumar da yin zagon kasa kan ayyukan da sojojin suke yi a yankin na kakkabe ayyukan ta'addanci da 'yan tada kayar baya a shiyyar," inda a ranar Juma'a ta ayyana janyewa daga matsayin da ta dauka a baya na haramtawa hukumar UNICEF gudanar da ayyukanta a shiyyar arewa maso gabashin kasar har na tsawon watanni 3, yankin wanda rikicin mayakan Boko Haram ya illata.

A cewar wasu bayanai na baya bayan nan, sojojin Najeriya sun gudanar da wani taron ganawa ne da wakilan hukumar ta UNICEF da yammacin ranar Juma'a.

A lokacin ganawar, sojojin sun shawarci wakilan hukumar da su guji aikata duk wani abu da zai iya haifar da koma baya wajen tattabar da tsaro a yankin, kana su nisanci yin kafar ungulu game da yakin da dakarun sojojin suke yi da ayyukan ta'addanci da masu tada kayar baya a yankin, in ji sanarwar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China