in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar Sin ta ce zargin da EU ta yiwa Sin na cewa wai ta tilasta a yi musanyar fasahohi ba shi da tushe
2018-12-21 16:30:29 cri
Tarayyar Turai wato EU ta yanke shawarar gabatar da korafinta kan kasar Sin ga kungiyar kasuwancin duniya wato WTO, na cewa, wai kasar Sin ta tilasta kamfanonin kasashen waje su yi musanyar fasahohinsu. Game da wannan batu, tawagar kasar Sin dake EU ta ce zargin da aka yiwa kasar Sin ba shi da tushe balle makama.

Tawagar kasar Sin ta bayyanawa kafofin watsa labarai cewa, a kasar Sin, babu wata doka ko daya da ta tilastawa kamfanonin kasashen waje su yi musanyar fasahohinsu. Bangarori biyu dake yin hadin-gwiwa da juna suna gudanar da musayar fasahohi ko kuma hadin-gwiwar fasahohi ne daidai wa daida bisa tushen samun moriyar juna, al'amarin da gwamnati ba za ta tsoma baki a ciki ba.

Tawagar kasar Sin ta kuma ce, kasar Sin ta yi kira da a daidaita sabanin ra'ayin kasuwancin kasa da kasa bisa tushen girmama juna gami da ka'idojin WTO.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China