in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
#Gyare-gyare da bude kofa# Xi: Ya kamata Sin ta aiwatar da tsauraran matakan da'a kan harkokin jam'iyyar kwaminis ta kasar daga dukkan fannoni
2018-12-18 12:36:07 cri
A wajen taron murnar cika shekaru arba'in da fara aiwatar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje wanda aka yi yau Talata a birnin Beijing, shugaba Xi Jinping ya bayyana cewa, kamata ya yi kasar Sin ta aiwatar da tsauraran matakan da'a kan harkokin jam'iyyar kwaminis ta kasar daga dukkanin fannoni, da kara kokarin inganta hadin-kai, da karfin yin kirkire-kirkire na jam'iyyar.

Xi ya ce, jam'iyyar kwaminis tamkar tushe ne na gudanar da harkokin kasar Sin yadda ya kamata, kuma ya kamata a tafiyar da harkokin jam'iyyar ta hanyar da ta dace kuma daga dukkanin fannoni. Xi ya ce, ya zama dole a karfafa hadin-gwiwar jam'iyyar, da kyautata shugabancinta nagari, da horas da kyawawan mahukuntan jam'iyyar, wadanda ke nuna biyayya da ladabi ga jam'iyyar kwaminis. Xi ya kuma ce, ya kamata a yi iyakacin kokarin kawar da dukkanin mutanen da suka aikata laifin cin hanci da karbar rashawa, da tabbatar da samun jami'an gwamnati masu rikon gaskiya da adalci, ta yadda za'a kirkiro wani yanayin siyasa mai tsabta, a ci gaba da aiwatar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China