Matashiyar wacce abubuwan fashewar dake jikinta suka tashi da ita a daidai lokacin da ta yi yunkurin wucewa ta gaban shingen binciken da jami'an tsaron suka kafa a Maiduguri, babban birnin jahar Borno dake shiyyar arewa maso gabashin Najeriya da yammacin ranar Laraba.
Babban jami'in hukumar 'yan sandan jahar Borno, Damian Chukwu, ya fadawa manema labaru cewa, ba'a samu rahoton jikkatan koda mutum guda ba.
Chukwu ya ce, ana zargin 'yar kunar bakin waken mayakan Boko Haram ne suka aika ta. (Ahmad Fagam)