in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta tabbatar da mutuwar mutane 15 da kuma ceto wasu 31 a ruftawar gini
2018-12-11 09:32:57 cri
Hukumomin bada agajin gaggawa a Najeriya sun sanar a jiya Litinin cewa mutane 15 ne suka hallaka kana wasu mutanen 31 kuma aka ceto su daga wani burabuzan wani bene mai hawa 7 wanda ya rufta a watan jiya a birnin Fatakwal mai arzikin mai dake kudancin kasar.

Ejike Martins, jami'in hukumar ba da agajin gaggawa na kasar NEMA ya bayyana cewa, "hakikanin abin da ya faru da ginin shi ne dukkan hawan benayen sun rufta ne daya bayan daya, matsalar da aka fuskanta shi ne dole ba za'a iya zakulo gawarwakin ba sai an bi sannu a hankali," Martins ya shedawa taron manema labarai a Fatakwal, babban birnin jihar Rivers.

Ginin, yana wani yanki ne wanda gwamnati ta kebe a babban birnin, wanda ake ci gaba da aikin gina shi makonni 3 da suka gabata bayan da ginin ya rufta.

Yadda masu aikin ceto suka gudanar da aikinsu ba tare da nuna kuzari ba ya haifar da cece kuce a tsakanin al'ummar yankin. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China