in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Kenya ta kaddamar da aikin kafa wata na'urar lantarki mai amfani da karfin hasken rana na farko a gabashin Afirka
2018-12-13 09:50:51 cri
Kasar Kenya ta zama kasa ta farko a yankin gabashin nahiyar da ta kafa na'urar samar da wutar lantarki mai amfani da karfin hasken rana, a babban filin saukar jiragen saman kasar, a wani mataki na rage hayaki mai gurbata muhalli da manyan jiragen sama ke fitarwa yayin tashi.

A jiya Laraba ne aka kaddamar da wannan na'ura mai karfin kilowatts 500 a filin tashi da saukar jiragen saman kasa da kasa na Moi dake birinn Mombasa dake gabar teku. Ana kuma fatan na'urar za ta rage a kalla tan 1,300 na hayaki mai gurbata muhalli da ke shiga sararin samaniya.

Shugaban hukumar kula da zirga-zirgar jiragen saman kasa da kasa Olumuyima Benard Aliu, ya ce wannan wani babban ci gaba ne ga bangaren zirga-zirgar jiragen saman kasar Kenya da ma nahiyar Afirka baki daya, baya ga fa'idar da za a girba daga wannan sabon canji da aka samu.

Ana kuma sa ran nau'rar za ta samar da Kilowatts dubu 820 na hasken wutar lantarki a shekara, za kuma ta rage a kalla tan 1,300 na hayaki mai gurbata muhalli a kowace shekara. Ana kuma fatan kasashe 14 za su rungumi wannan tsari, kasashe 12 daga yankin Afirka ne sai kuma kasashe 2 daga yankin Karebiya. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China