in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD: Masu aikin jin kai na matsa kaimin aiki a yankunan Kamaru masu fama da tashin hankali
2018-11-22 09:40:46 cri
Kakakin MDD Stephane Dujarric, ya ce masu aikin jin kai na kara fadada ayyukan su, a yankunan kasar Kamaru dake fama da tashe tashen hankula, inda suke tallafawa a kalla mutane 437,000 dake samun mafaka a wasu sansanoni dake cikin kasar.

Stephane Dujarric, ya ce ofishin MDD dake lura da 'yan gudun hijira ko OCHA, da abokan huldar sa, na kara kaimi wajen taimakawa fararen hula da rikici ya raba da muhallan su, a yankunan kudu maso yammaci da arewa maso yammacin kasar. Ya ce hukumar OCHA ta yi korafi game da karancin tsaro a yankunan biyu, da kuma karancin kudaden gudanar da ayyuka yadda ya kamata.

OCHA ya ce bisa wasu rahotanni, shirin tallafi na kasar Kamaru, wanda aka yi hasashen zai lashe kudi har dalar Amurka miliyan 320, ya gamu da gibin kusan kaso 37 bisa dari, yayin da ayyukan gaggawa da aka yi hasashen za su bukaci kudi har dala miliyan 15, domin tallafawa mutane kusan 160,000, suka samu kudi da bai wuce dala miliyan 5 kacal ba.

Tun daga shekarar bara ne dai 'yan aware a kasar ta Kamaru, ke kaddamar da hare hare a yankunan dake amfani da turancin Ingilishi a yankunan arewa maso yamma da kudu maso yammacin kasar, a wani mataki da suka ce martani ne, bisa wariya da tsagin 'yan kasar mafiya rinjaye masu amfani da yaran Faransanci ke nuna masu. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China