in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An saki dalibai 79 da aka sace a kasar Kamaru
2018-11-07 19:32:56 cri
Mai magana da yawun gwamnatin Kamaru kana ministan sadarwar kasar Issa Tchiroma ya bayyana cewa, an saki 'yan makaranta 79 da direba guda da aka sace a wata makarantar sakandare mai zaman kanta a yankin arewa maso yammcin kasar da ake magana da Turancin Ingilishi mai fama da tashin hankali. Amma kuma har yanzu shugaban makarantar da wani malami guda na tsare a hannun wadanda suka yi garkuwa da su.

Tchiroma ya ce, daga bisani yaran sun hadu da iyayensu.

Kakakin rundunar sojojin kasar ta Kamaru, Kanar Didier Badjeck, ya ce an saki mutane 80 da ake garkuwa da su ne a safiyar yau Laraba, bayan wani samame da sojojin suka kaddamar a Bafut, wani kauye dake wajen Bamenda,babban birnin yankin arewa maso yammacin kasar.

A ranar Lahadi da dare ne dai aka sace daliban da malamansu a yankin arewa maso yammacin kasar, daya daga cikin yankunan da ake magana da Turancin ingilishi mai fama da tashin hankali.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China